Tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma sanata mai wakiltar mazabar Zamfara ta yamma, Abdulaziz Yari Abubakar, ya baiwa ‘yan asalin jihar 1,700 tallafin karatu a jami’o’in Najeriya daban-daban.
Shugaban kwamitin shirin bayar da tallafin karatu na A.A Yari, Sanata Tijjani Yahaya Kaura, ya shaida wa manema labarai a wani taron manema labarai cewa, an kaddamar da shirin ne a kokarinsa na daukaka darajar ilimi a jihar.
Ya ce a karkashin shirin, za a tantance wadanda suka cancanta daga gidaje marasa galihu wadanda iyayensu ba za su iya daukar nauyin ‘ya’yansu zuwa manyan makarantu ba.
Kaura ya ce za a ba wa duk wadanda suka ci gajiyar tallafin karatu a fadin jihar ba tare da la’akari da bambancin addini ko jam’iyyar siyasa ba.
A cewarsa, kwamitin shirin bayar da tallafin karatu na A.A Yari ya kammala shirin fara rabon fom ga wadanda suka ci gajiyar shirin a karkashin kwamitin gudanarwa na kowace kananan hukumomi 14 na jihar.