Kasa da sa’o’i 24 da hawan kujerar shugabancin jihar Kano, da sanyin safiyar Talatar nan ne Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kori Babban Sakataren Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar, Muhammad Abba Danbatta.
Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature, ya tabbatar da hakan a safiyar ranar Talata ta wata sanarwa da ya ba wa manema labarai
Ya kuma bayyana cewa gwamna Yusuf ya amince da nadin Alhaji Laminu Rabiu a matsayin sabon sakataren zartarwa na hukumar alhazai ta jihar.