A lura sosai game da yadda jabun takardun naira suka yawaita—CBN ya gargadi ƴan Najeriya

Babban bankin Najeriya, CBN, ya gargadi ‘yan Najeriya da su yi hattara da kudaden Naira na bogi da ke yawo ba bisa ka’ida ba.

Wannan gargadi na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mukaddashin daraktan sadarwa na CBN, Hakama Sidi Ali, ta fitar a Abuja ranar Juma’a.

“An jawo hankalin Babban Bankin na CBN a kan yadda ake yada takardun kudi na jabu, musamman manyan kuɗaɗen da wasu mutane ke yi,” in ji ta.

Sidi Ali ya te jabun na Naira an fi amfani da shi wajen hada-hadar kasuwanci a kasuwannin abinci da sauran cibiyoyin kasuwanci a fadin manyan kasuwanni a garuruwan kasar.

Ta ce duk wanda aka samu da hannu wajen shigar da kudaden na jabu to zai fuskanci hukunci mai tsanani.

Draktar ta ce dokar ta tanadi hukuncin zaman gidan yari wanda ba zai yi kasa da shekaru biyar ba, ga duk wanda aka samu da laifin yin jabun kudin Naira ko kuma duk wata takardar doka a Najeriya.

“CBN na ci gaba da hadin gwiwa da hukumomin tsaro da wadanda suka dace domin kwato takardun kudin Naira na bogi, kamawa da hukunta masu yin jabun.”

“Ana kuma kara kira ga jama’a da su kai rahoton duk wanda ake zargin yana da kudin jabun naira ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa, reshen CBN, ko ta contactcbn@cbn.gov.ng,” in ji ta.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...