Zaben Najeriya:An soma fafatawa tsakanin Atiku da Buhari

Buhari da Atiku

Ranar Lahadi ne aka buga kugen siyasa a Najeriya inda ‘yan takara a matakin tarayya za su soma yakin neman zaben 2019 gadan-gadan.Dokokin hukumar zaben kasar, INEC, sun nuna cewa 18 ga watan Nuwamba 2018 ita ce ranar da a hukumance za a soma yakin neman zaben.Mutum 78 ne ke takarar shugaban Najeriya, sai dai masana na ganin fafatawar za ta fi yin zafi ne tsakanin Shugaba Muhammadu Buhari na jam’iyyar APC da tsohon mataimakin shugaban kasar Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP. Dukansu biyu shekarunsu na haihuwa sun wuce 70.Shugaba Buhari ya ce zai nemi wa’adi na biyu na shugabancin kasar ne saboda “na kammala ayyukan da na soma.”Shugaban, wanda ya kayar da Shugaba na wancan Goodluck Jonathan a zaben 2015, ya gina takararsa ne kan abubuwa uku: wanzar da tsaro, samar da ayyuka da kyautata tattalin arzikin kasar, da kuma yakar rashawaMasana harkokin tsaro da dama irinsu Malam Kabiru Adamu sun amince cewa shugaban ya samu gagarumar nasara a fannin tsaro – musamman a yaki da kungiyar Boko Haram wacce ta kashe dubban mutane sannan ta raba miliyoyi daga gidajensu.


Atiku Abubakar ya sha alwashin samar da ayyuka sai dai wasu na zarginsa da cinhanci da rashawa, ko da yake ya musanta zargin.

Sai dai sun nuna gazawar shugaban wajen shawo kan matsalolin masu satar mutane don karbar kudin fansa da rikicin namona da makiyaya – wadanda suka yi kamari a shekarun baya bayan nan.

Kazalika an sha caccakar Shugaba Buhari saboda gaza yin tagomashi kan inganta tattalin arzikin Najeriya, ko da yake gwamnatinsa ta sha cewa zai dauki lokaci kafin kasar ta warke daga masassarar tattalin arzikin da ta fada a ciki lokacin da ta karbi mulki, kamar yadda ministar kudi Zainab Ahmed ta jaddada a hirar ta da BBC a makon jiya.Sake gina Najeriya

Shugaba Buhari ya ce ya kama barayi amma ‘yan hamayya sun ce masu adawa da shi kawai yake kamawa.
A nasa bangaren, Alhaji Atiku Abubakar, ya sha alwashin sake gina Najeriya ta hanyar warware matsalolin tattalin arzikin da take ciki.Tsohon mataimakin shugaban kasar, wanda ya ce ya kware wajen kasuwanci da samar da ayyuka, ya yi alkawarin sama wa matasa ayyuka da inganta tsaro.Sai dai gwamnatin Buhari da magoya bayanta sun sha sukar Atiku Abubakar wanda suke zargi da cinhanci da rashawa, zargin da yake musantawa.A matakin jihohi, wata kididdiga da jaridar Daily Trust ta yi ya nuna cewa mutum 821 ne ke takarar gwamna a jiha 28 da za a gudanar da zabe. Nan gaba ne dai za a soma yakin neman zaben gwamnoni.INEC ta gargadi masu takara a dukkan matakai kan tsaftace kalamansu lokacin yakin neman zabe tana mai yin alwashin duk wanda ya keta dokokinta.

More from this stream

Recomended