Shettima ya dawo Najeriya bayan ziyarar aiki kasashen Guinea da Switzerland

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya dawo gida birnin tarayya Abuja bayan ya shafe kusan mako guda a kasashen Guinea Conarkry da kuma Switzerland.

Shettima ya sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja da ya wakilci shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu a wurin bikin rantsar da, Mamadi Doumbouya shugaban kasar Guinea da kuma jagorantar tawagar Najeriya a a wurin taron tattalin arziki na duniya da aka yi birnin Davos na kasar Switzerland da aka saba gudanarwa a kowace shekara.

Bayan saukarsa a Najeriya Shettima ya bayyana cewa Najeriya ta sake kwato matsayinta na kujerar kan gaba a tattaunawa da suka shafi tsare-tsare a matakin yankin nahiya

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]