Tsohon ministan yan sanda Adamu Waziri  ya koma jam’iyar ADC daga PDP

Adamu Maina Waziri, tsohon ministan yan sanda ya sanar da ficewarsa daga jam’iyar PDP.

Waziri wanda na daya daga cikin wadanda aka kafa jam’iyar PDP da su kuma mamba ne a kwamitin amintattun jam’iyar ya sanar da daukar matakin barin jam’iyar PDP a ranar Litinin a mazabar Dogo Tebo dake karamar hukumar Potiskum ta jihar Yobe.

Ya alakanta barin jam’iyar da halin da ake ciki a yanzu da kuma samawa kasar makoma kyau.

A cewar tsohon ministan shugabancin jam’iyar PDP da ake da shi a yanzu bai yi dai-dai da irin wanda ya dace da babbar jam’iyar siyasa ba.

Ya kara da cewa nan take ya koma jam’iyar African Democratic Alliance (ADC) nan take.

A yan makonni jam’iyar PDP ta fuskanci sauya sheka daga cikinta da wasu manyan yan siyasa su ka yi ya zuwa APC da ADC.

More from this stream

Recomended