Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Je Bauchi Ta’aziyya Wa Gwamnan Jihar

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci tawagar gwamnatin jiharsa zuwa Jihar Bauchi domin mika ta’aziyya ga Gwamna Bala Mohammed, wanda ya rasa abokiyar zaman mahaifiyarsa kwanan nan.

A jawabinsa, Gwamna Yusuf ya bayyana marigayiyar a matsayin mace mai kyawawan halaye da jajircewa, wacce ta bayar da muhimmiyar gudunmawa ga iyalanta da al’ummarta.

Ya ce: “Muna roƙon Allah Madaukakin Sarki ya gafarta mata, ya sanyata a cikin Aljanna Firdausi, kuma ya bai wa iyalanta ƙarfin hali don jure wannan babban rashi.”

Ziyarar ta’aziyyar ta nuna zumunci da goyon baya tsakanin jihohin Kano da Bauchi a irin wannan lokaci mai cike da alhini.

More from this stream

Recomended