Soja ya bindige yan bindiga biyu da suka kai hari akan hanyar Abuja

Biyo bayan harin da aka kai kan shingen binciken ababen hawa a kusa da Dutsen Zuma wani jarimin soja ya samu nasarar kashe yan bindigar biyu kafin shima ya mutu.

A ranar Alhamis ne da misalin karfe 08:00 na dare yan bindiga suka kai hari kan shingen binciken rundunar sojan Najeriya Bataliya ta 102 inda suka gamu da turjiya mai karfi daga sojojin.

A cewar wata majiya dake kusa da wurin bayan da yan bindigar suka gaza samun nasara sun sulale sun saje cikin al-ummar garin Gauraka dake kusa da wurin a bin da ya haifar da rudani.

Jami’in sojan shi ne yake aikin sanya idanu a shingen lokacin da lamarin ya faru inda ba kuma tare da bata lokaci ba ya fara mayar da wuta a yayin harin.

Lamarin dai ya jawo cinkoson ababen hawa a babbar hanyar da ta hada Abuja da Kaduna.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]