Ɗalibin jami’a ya yi yunkurin kashe kansa kan sakamakon kammala karatu da aka riƙe masa tsawon shekaru 5

Wani ɗalibi da ya kammala Jami’ar Ambrose Ali(AAU) dake Ekpoma a jihar Edo ya yi yunkurin hallaka kansa bayan da ya zargi jami’ar da kin bashi takarardar sakamakon kammala karatu.

Ɗalibin mai suna Precious Ogbeide ya kammala karatu a Jami’ar a shekarar 2018 amma ya koka cewa ba a bashi takarardar kammala karatu ba.

Jaridar Punch ta rawaito cewa iyayen Ogbeide sun bayyana cewa ya dadde yana fama da matsananciyar damuwa saboda rashin karbar shedar kammala jami’ar bayan da ya shafe shekaru biyar yana karatu.

Ɗalibin ya rika kekketa jikinsa da guntun fasasshiyar kwalba.

Suma wasu tsofaffin daliban jami’ar sun koka kan yadda har yanzu jami’ar ta gaza basu shedar kammala karatu.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...