Ƴansanda sun kama mutumin da yake lalata da ƴar cikinsa

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ogun sun kama Ibrahim Aliu mai shekaru 41 a duniya a Papa Olosun, Oja Odan a karamar hukumar Yewa ta Arewa bisa zarginsa da lalata da ‘yarsa mai shekaru 12 (an sakaya sunanta).

 
An kama Aliu ne a ranar Alhamis bayan matarsa, Temitope Egbebi, ta kai kara ofishin ‘yan sanda na Oja Odan.

 
Egbebi ta yi zargin cewa Aliu yana lalata da yarinyar a duk lokacin da ta ziyarce shi a lokacin hutu.

 
Ta shaida wa ’yan sanda cewa ta gano hakan ne bayan kai yarinyar zuwa Asibitin Jihar da ke Ilaro domin a duba lafiyarta da kuma jinyar yadda wani ruwa ke fita daga al’aurarta.

 
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Omolola Odutola, ta bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

More News

Magoya bayan jam’iyar NNPP sun ƙona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

Magoya bayan jam’iyar NNPP sun ƙona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

PDP ta ɗauki hanyar warware rikicin jam’iyar

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya ce  an kawo karshen rikicin cikin gida da ya dabaibaye jami'yar PDP. Mohammed wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin...

Dakarun Najeriya sun cafke wasu ƴan’aiken ƴanbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...