Ƴansanda sun kama mutane sama da mutane 30 saboda ta’amali da miyagun ƙwayoyi a Gombe

Akalla mutane 31 ne rundunar ‘yan sandan jihar Gombe ta kama a yayin da take gudanar da samame kan maboyar masu safarar ƙwayoyi.

Da yake bayyana hakan a ranar Alhamis, jami’in hulda da jama’a na rundunar, ASP Mahid Abubakar, ya ce hedkwatar ‘yan sandan jihar Gombe ta hannun tawagarta ta ‘yan sintiri ta 999 sun kai samame kan wasu masu aikata laifuka inda aka kama su.

Ya bayyana cewa, samamen ya kai ga kamawa tare da dawo da wadanda ake zargi da shan miyagun kwayoyi.

A cewarsa, “A kokarin da ake yi na kare lafiyar jama’a da kuma yaki da miyagun ayyuka, da misalin karfe 10:00 na dare, tawagar, karkashin jagorancin jami’ai masu himma, ta kama mutane tara da ake zargin suna da hannu a ayyukan da suka shafi muggan kwayoyi.

“Daga cikin abubuwan da aka kwace akwai busassun ganyen da aka yi imanin cewa wiwi ne da kuma sauran abubuwa.”

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...