Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a yankin Ibeju-Lekki da ke jihar a ranar Juma’a.

Wadanda ake zargin sun hada da Victor Okoman mai shekaru 24, Saheed Balogun mai shekaru 38 da kuma David Kaimon mai shekaru 27.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Legas, Benjamin Hundeyin, babban Sufeton ‘yan sandan ne ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafin sa na X (Twitter a baya), da yammacin Juma’a.

“Jami’an sashen Elemoro sun amsa kiran gaggawa a yau, Juma’a, 20 ga Satumba, 2024, da misalin karfe 0200 na safe kimanin wasu matasa uku da suka yi wa masu wucewa fashi da bindiga, inda suka kama Victor Okoman mai shekaru 24, Saheed Balogun mai shekaru 38 da David Kaimon, mai shekara 27 dauke da wata karamar bindiga mai dauke da kayan alburusai,” in ji Hundeyin.  

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar ya kara da cewa wadanda ake zargin sun jagoranci ‘yan sanda wajen kwato alburusai guda 26.

Ya kara da cewa ana ci gaba da bincike kan lamarin.

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...