Ƴan ta’adda sun sace sama da mutum 100 a Zamfara saboda sun kasa biyan harajin da suka ɗaura musu

Wasu ‘yan bindiga sun sake yin garkuwa da mutane sama da 100 a garuruwan Mutumji, Sabongari Mahuta, Kwanar Dutsi da Unguwar Kawo da ke karamar hukumar Maru a jihar Zamfara saboda rashin biyansu kudaden harajin da aka dora wa ƴan ƙauyukan.

An tattaro cewa ‘yan bindigar na addabar al’umma saboda ba za su iya biyan harajin da aka dora musu ba.

Wani mazaunin garin Mutumji, Alhaji Muhammad Usman ya ce ‘yan bindigar sun far wa al’ummar ne da misalin karfe 8 na dare inda suka fara harbe-harbe ba da dadewa ba, lamarin da ya tilasta wa mazauna garin gudu domin tsira.

A cewar wani dan kauyen, shugaban ‘yan fashin da ke yankin, Damina, a baya ya sanya wa al’ummar yankin Naira miliyan 110 a matsayin haraji, inda ya ba su wa’adin mako biyu su bi ko kuma su fuskanci sakamakon da zai biyo baya.

“An dorawa al’ummarmu harajin N50m, yayin da aka dora N30m a Kwanar Dutsi; N20m akan Sabongari Mahuta, da N10m akan Unguwar Kawo”, in ji shi.

Wata majiya daga yankin ta ce al’ummar yankin sun fara bayar da wadannan kudade ne a lokacin da ‘yan ta’addan suka far wa jama’ar da yammacin ranar Juma’a.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...