Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Larabar da ta gabata, ta ce tana kan gaba a halin da ake ciki dangane da sace dalibai mata biyar na Jami’ar Tarayya Dutsinma, jihar Katsina.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, ASP Abubakar Sadiq, ne ya bayyana hakan a cikin wata ‘yar gajeruwar sanarwa a ranar Laraba, inda ya ce rundunar ta tura kayan aiki da nufin ceto wadanda lamarin ya rutsa da su, tare da kamo wadanda suka aikata wannan danyen aiki yayin da ake ci gaba da bincike.
“A ranar 4 ga Oktoba, 2023, da misalin karfe 2 na safe, wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne sun yi garkuwa da wasu dalibai mata biyar na jami’ar tarayya ta Dutsinma.
“Rundunar ta na kan gaba wajen lamarin, domin ta yi amfani da duk wata dabarar aiki da nufin ceto wadanda abin ya shafa.”