Ƴan sanda sun kama wani kasurgumin dan daba a Bauchi

Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kama wani da ake zargin ya cire hannun wani matashi dan shekara 25 tare da daba masa wuka a kai.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Ahmed Wakil, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, ya ce wanda ake zargin ya kasance cikin jerin sunayen ‘yan sanda na tsawon shekaru biyu da ake nema ruwa a jallo bisa laifin dabanci da kuma haddasa mummunar barna.

Ya ce wanda ake zargin ya aikata laifin tare da wasu mutane biyu.

Ya kara da cewa, dubunsa ta cika ne a lokacin da ‘yan sandan da ke sintiri suka kai samame a wata maɓoya a wata unguwa da ke wajen birnin Bauchi suka kama shi.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A ranar Asabar 22 ga Yuli, 2023 da misalin karfe 6:30 na yamma, jami’an ‘yan sanda da ke hedikwatar ‘C’ Divisional hedkwatar ‘C’, a lokacin da suke aikin sintiri, suka gano tare da kai samame a wata maɓoya da ke Sabon Layi da ke wajen birnin Bauchi, wanda ya kai ga kama wani mutum mai suna Muhammad Abdullahi, wanda aka fi sani da Luwawu.”

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...