Ƴan sanda sun kama wacce ta lakaɗa wa mahaifiyarta duka

Rundunar ‘yan sandan Najeriya (NPF), ta kama wata mata ‘yar jihar Anambra da ke yi wa mahaifiyarta tsohuwa duka.

An dauki hotonta ne a cikin wani faifan bidiyo tana dukan mahaifiyarta mai shekaru da dama tare da watsa mata bokitin ruwa.

Kakakin rundunar ƴan sanda a Jihar Anambra, Ikenga Tochukwu, ya tabbatar wa manema labarai damke matar a ranar Lahadi.

Tochukwu ya bayyana cewa wanda ake zargin ta yi wa mahaifiyarta mai shekaru 75 bulala.

Ya ce: “An kama wanda ake zargin da yi wa tsohuwa bulala a kai a kai tare da watsa mata ruwa a kwance a kasa, an kama ta kuma an tsare ta domin gurfanar da ita.”

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...