Ƴan sanda sun kama riƙaƙƙen ɓarawon awaki a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta ce jami’anta sun kama wani da ake zargin barawo ne da ya kware wajen satar awaki a kauyen Pasali Konu da ke karamar hukumar Kagarko a jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mansur Hassan, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Najeriya ranar Lahadi a Kaduna cewa an kama wanda ake zargin ne a ranar Asabar.

Hassan ya ce, a ranar 11 ga watan Nuwamba da misalin karfe 0430, wata tawagar sa ido da ‘yan banga, yayin da suke aikin sintiri a kauyen, sun kama matashin mai shekaru 20 da haihuwa.

A cewarsa, wanda ake zargin ya fito ne daga kauyen Igwa na karamar hukumar Kagarko.

“Wanda ake zargin, wanda ya kware wajen satar awaki, ya amsa cewa su biyu ne da suka zo kauyen domin satar awaki,” in ji Hassan.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...