Ƴan sanda sun kama dan damfara a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta kama wani da ake zargin dan damfara ne da ya kware wajen damfarar jama’a wadanda ba su ji ba gani ba ta hanyar amfani da kudin jabu.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, ASP Abubakar Sadiq, ya ce ‘yan sanda sun samu nasarar cafke wanda ake zargin, Bishir Umar mai shekaru 28, wanda aka fi sani da Dan Zamfara daga karamar hukumar Magamar Jibia, a lokacin da rundunar ta samu bayanan sirri kan ayyukansa da kuma inda ya ke.

“Bayan an binciko shi nan take aka kama shi, an kwato wasu kudade na jabu daga hannun sa, guda hudu na N1000, CFA 10,000 na jamhuriyar Nijar, da takardar 2000 na CFA na jamhuriyar Nijar,” in ji ASP Sadiq.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Katsina, ya ce wanda ake zargin a yayin gudanar da bincike, ya amsa laifin aikata laifin.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...