Ƴan bindiga sun saki yaron da suka yi garkuwa da shi na tsawon shekaru 2

Masu garkuwa da mutane sun sako yaro na karshe Treasure Ayuba da suka yi garkuwa da shi a makarantar sakandare ta Bethel Baptist da ke jihar Kaduna bayan shafe shekaru biyu da watanni hudu a hannunsu.

Treasure na cikin dalibai 121 na makarantar Baptist da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a Yuli 2021 a kauyen Maraban Damishi a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.

An ce an sake shi a ranar Juma’a tare inda tuni ya koma ga ƴan’uwansa.

A halin da ake ciki gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya bayyana farin cikinsa da samun ‘yanci daga hannun masu garkuwa da mutane.

Gwamna Sani ya bayyana jin dadinsa ga jama’a da hukumomi da suka jajirce wajen yin kokari da addu’o’i na ganin an dawo da wanda aka sace.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...