Ƴan bindiga sun kashe wani Farfesa a jihar Delta

Ƴan bindiga sun kashe Farfesa Emeka Chukwuma wani malami a jami’ar jihar Delta dake garin Abraka.

A cewar jaridar Punch, Farfesa Chukwuma mai shekaru 56 ya dawo gidansa dake Umueji a Asaba babban birnin jihar Delta  ranar Juma’a domin yin hutun ƙarshen mako da ya saba yi amma a wannan karon sai ƴan bindiga suka bindige shi har lahira.

“An kashe Prof Emeka  Chukwuma ranar Juma’a da daddare a Asaba malami ne a jami’ar jihar Delta dake Abraka, ” a cewar wata majiya da ta gana da jaridar ta Punch.

“Prof Chukwuma ya saba zuwa gida a duk ƙarshen mako. Amma cikin rashin sa’a ya dawo jiya hutunsa na ƙarshen mako amma sai aka kashe shi a gidansa.”

” A yanzu da nake magana da kai babu tsaro a Asaba. Mun shiga ruɗu kan halin da ake ciki.”

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar, Bright Edafe bai ce komai ba da aka nemi jin ta bakinsa.

More from this stream

Recomended