Ƙasashen Kuwait da Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) sun bayyana cewa har yanzu suna fuskantar hare-haren jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami da aka harba daga Iran, duk da tsagaita wutar da aka cimma kwanan nan.
Rundunar sojin Kuwait ta ce garkuwar tsaron sararin samaniyya ta hana wani yunƙuri na jirage marasa matuka daga Iran, inda wasu daga cikin jiragen ke nufar wuraren haƙar mai da tashoshin wutar lantarki.
Ma’aikatar harkokin cikin gida ta UAE ta bayyana cewa tana tinkarar wata barazanar makamai masu linzami.
Ƙasashen yankin Gulf sun yi maraba da tsagaita wutar, sai dai Oman, wadda ta taka rawa wajen shiga tsakani, ta jaddada bukatar gudanar da tattaunawa mai mahimmanci domin samar da zaman lafiya mai dorewa.
Ƙasashen Kuwait Da UAE Na Fuskantar Hare-Haren Iran Duk Da Tsagaita Wuta

