Ɗan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da jakar da ta bata mai dauke da sama da Naira miliyan 100.

A ƙarshen taron wa’azi na musamman da aka gudanar a Bauchi, Daraktan kungiyar Agaji ta farko na kasa Engr Mustapha Imam Sitti ya yabawa Kankia bisa gaskiyarsa.

Kungiyar JIBWIS reshen jihar Bauchi ta bayyana a shafinta na sada zumunta na Facebook cewa Kankia ya gano jakar kuma ba tare da bata lokaci ba ya kai rahoto ga ‘yan sanda. 

Mai shi ya tabbatar da cewa babu abin da ya ɓace a cikin kuɗin.

Bisa la’akari da gaskiyarsa, kungiyar Izala ta karrama Kankia da lambar yabo da kuma daukar nauyinsa a  aikin hajjin bana.

Ya kuma karbi Naira miliyan biyu daga hannun Hon.  Abdulmalik Zannan Bangudu da motar bas daga Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed domin fara harkar kasuwanci.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...