Ɗalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin wutar lantarki a wuraren kwanansu.

Daliban sun kulle kofar makarantar, suna rera wakokin hadin kai tare da nuna kwalaye masu rubuce-rubuce daban-daban kamar, ‘Babu hasken da za a jika Garri’ da “Ba mu da SUG” yayin da wasu kuma suka rike bokitin da babu ruwa a ciki domin nuna rashin ruwa a makarantar. 

Daliban sun koka da yadda lamarin ya janyo musu wahalhalu da kuma illa ga ayyukansu na neman ilimi.

Haka kuma an kulle da yawa daga cikin ma’aikata da shugabannin jami’ar a wajen kofar makarantar, inda aka hana su shigowa.

Sai dai babban jami’in kula da harkokin dalibai na Jami’ar, Farfesa Christopher Piwuna, ya tabbatar da kalubalen karancin ruwa da kuma katsewar wutar lantarki a gidajen daliban.

Ya kuma ɗora alhakin lamarin a kan Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Jos a kan wani bashin da yake bi.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...