Ƴan sanda sun kama mutane 4 masu garkuwa da mutane a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta ce jami’an tsaro sun kama wasu mutane huɗu da ake zargin ƴan fashin daji ne dake addabar birnin.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Lahadi, mai magana da yawun rundunar ƴan sandan birnin, Josephine Adeh ta ce an kama mutanen ne a ranar 7 ga watan Yuni a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ya haɗa da sojojin dake tsaron fadar shugaban, jami’an DSS, mafarauta da kuma ƴan sanda.

Adeh ta ce jami’an tsaro sun yi amfani da bayanan sirri inda suka farma wasu sanannun sansanin masu garkuwa da mutane dake Gidan Dogon da kuma Dajin Kweti dake Kaduna kan iyaka da Abuja inda suka bi sawun mutanen suka kuma kama su.

Ta ce mutanen da aka kama sun haɗa da Yahaya Abubakar mai shekaru 25; Mohammed Mohamed, mai shekaru 32, wanda tsohon mai laifi ne ; Umar Aliyu, mai shekaru 20; da kuma  Nura Abdullahi mai shekaru 32 wanda shima tsohon mai laifi ne.

Mutanen sun amsa laifin kasancewa mambobi na ƙungiyar masu garkuwa da mutane da sukewa kansu laƙabi da ‘Mai One Million’ wanda su ne da alhakin garkuwa da mutane da dama Abuja da kewayenta.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...