Ƴan sanda sun kama mai garkuwa da mutane da ya kashe ɗan gidan ASP na ƴan sanda

Rundunar ƴan sandan jihar Bauchi ta kama wani mai suna, Rabi’u Adamu da ake zargi da yin garkuwa da kuma kisan wani yaro ɗan shekara 12 ɗan gidan ASP Bala Yarima.

A wata sanarwa ranar Juma’a, mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar,Ahmed Wakili ya ce wanda ake zargi mai shekaru 21 ya yi garkuwa tare da kashe Christopher Musa dake garin Magaman Gumau.

Wakili ya ce anyi garkuwa da marigayin ranar ranar 21 ga watan Maris lokacin da aka aike shi.

” A ranar 21 ga watan Maris 2024 da ƙarfe 08:00 na safe rundunar ƴan sandan jihar Bauchi ta samu kiran kai ɗaukin gaggawa na yin garkuwa da Christopher Bala ɗan gidan ASP Bala Yarima a garin Gumau,” a cewar sanarwar.

Biyo bayan binciken farko da aka yi wanda ake zargin ya amsa laifin shaƙe wuyan Christopher har ya mutu kuma ya amsa laifin  tatsar kuɗi har naira 200,000 daga mahaifin yaron.

Wanda ake zargin ya ce bayan da ya fuskanci cewa marigayin ya gane shi hakan ne ya sa ya kashe shi inda ya binne shi kusa da wani tsauni dake ƙauyen Bazale.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...