Ƴan sanda na bincike kan mutuwar mutane uku ƴan gida ɗaya a Kwara

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kwara, Victor Olaiya, ya bayar da umarnin gudanar da sahihin bincike kan mutuwar wasu ‘yan’uwa guda uku da suka mutu a cikin mota da ke tsaye a garin Ilorin  babban birnin jihar.

Lamarin dai ya faru ne a ranar Lahadi da ta gabata.

A cewar wani mazaunin unguwar, ’yan sandan sun kasa shiga ginin saboda kofar a kulle da kwaɗo take, kuma babu kowa a gidan.

Rahotanni sun nuna cewa daga bisani ‘yan sandan sun zarce zuwa gidan mahaifiyar marigayiyar da ke kan titin Taiwo Isale, Ilorin, inda take ta jimami bayan ta suma sakamakon mutuwar ‘ya’yanta a ranar Lahadi. 

Ƴan sandan sun tambayi uwar a kan  me ya sa ba ta kai rahoton lamarin a hukumance gare su ba.

More News

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...

Gwamnati za ta fara biyan ma’aikata naira 30,000 mafi ƙarancin albashi a Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya sanar da cewa za su fara aiwatar da tsarin mafi ƙarancin albashi naira 30,000 ga ma'aikatan jihar...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...