Ƴan sanda a Kano sun kama wani ɗan daba da ya kashe wani matashi

Jami’an ƴan sanda a jihar Kano, sun samu nasarar kama wani ɗan daba da ya kashe wani matashi a unguwar Dorayi dake birnin Kano.

Matashin mai suna Abba Garba wanda aka fi sani da Ɗan Ƙuda dake zaune a unguwar Ɗorayi Chiranchi ana zarginsa da  kashe wani matashi mai suna, Zahraddeen Iliyasu ta hanyar caka masa wuƙa a wuya bayan da suka samu saɓani.

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.

Ya ce an kama matashin ne lokacin da yake ƙoƙarin tserewa ya zuwa ƙasar Jamhuriyar Nijar.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...