Ƴan bindiga sun sace wasu ɗalibai a jihar Delta

Rahotanni na cewa ƴan bindiga sun sace dalibai da kawo yanzu ba a san yawan adadinsu ba akan babbar hanyar east-west a ƙaramar hukumar Ughelli ta jihar Delta..

A cewar jaridar The Cable ɗaliban dake cikin mota ƙirar Sienna na kan hanyarsu ta dawowa daga birnin Calabar ne  na jihar Cross River lokacin da aka farma motar ta su da yammacin ranar Juma’a.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Delta,Bright Edafe shi  ne ya tabbatarwa da jaridar faruwar haka a ranar Litinin.

Edafe ya ce jami’an ƴan sanda na bin sawun masu garkuwar domin kuɓutar da ɗaliban.

Lamarin ya shiga jerin ƙarin yawan ɗaliban da aka yi garkuwa da su a Najeriya.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...