Ƴan bindiga sun kashe jami’in NDLEA tare da yin garkuwa da mutane 3 a Sokoto

Wasu ƴan bindiga da ba’asan ko suwaye ba sun harbe wani jami’in hukumar NDLEA dake hana sha da kuma fataucin miyagun ƙwayoyi kana suka kuma yi garkuwa da wasu mutane 3 akan titin zuwa filin jirgin saman Sultan Abubakar dake Sokoto.

Wani mazaunin yankin da abun ya faru, Muhammad Baba Usman wanda ɗansa na daga cikin waɗanda aka sace ya ce ƴan bindigar sun kai harin ne da misalin ƙarfe 09:30 na dare.

“Su huɗu ne dukkaninsu ɗauke da bindiga. Sun zo a cikin mota da suka ajiye ta a bakin titi.Dukkansu sun fito suka fara harbin kan me uwa da wabi mutum guda harsashi ya sama ya kuma mutu akan hanyar zuwa asibiti,”

“Sun kuma yi awon gaba da mutane uku ciki har ɗa na. Har yanzu muna jiran kiran wayarsu muji abun da za su buƙata.” A cewar Muhammad

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Sokoto, ASP Ahmed Rufa’i ya tabbatar da cewa wanda ya mutu ma’aikci ne a hukumar NDLEA.

A cewar Rufa’i ƴan sanda na bin sawun masu garkuwa da mutanen.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...