Zulum zai bayar da tallafin karatu ga ƴan asalin Jihar Borno

Gwamnatin jihar Borno ta ce an kammala shirye-shiryen bayar da tallafin karatu na musamman ga dalibai marasa galihu da ke karatun aikin jinya da ungozoma.

Babban sakataren hukumar bayar da tallafin karatu ta jihar Borno, Mallam Bala Isa ne ya bayyana haka a Maiduguri ranar Juma’a.

“Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum na bayar da tallafin karatu na musamman ga ‘yan asalin jihar Borno masu sha’awar karatun aikin jinya da ungozoma.

“Masu neman dole ne su sami maki a Turanci, Maths, Biology, Chemistry da Physics a jarabawar gama sakandare ta WAEC, NECO ko NABTEB.”

Isa ya ce duk masu sha’awa su mika takardar shaidarsu ga hukumar bayar da tallafin karatu kafin ranar 2 ga watan Agusta.

Idan dai ba a manta ba Zulum ya yi jawabin kaddamar da wa’adi na 2, inda ya bayyana shirin gina karin makarantun koyon aikin jinya da ungozoma guda biyu a jihar domin samar da karin ma’aikata a bangaren lafiya.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...