Zaben Osun: Saraki ya ziyarci dantakarar jam’iyar SDP, Omisore

Shugaban majalisar dattawa, Abubakar Bukola Saraki, ya ziyarci Iyiola Omisore dan takarar gwamnan jihar Osun karkashin jam’iyar SDP a zaɓen da aka gudanar ranar Asabar.

Ganawar tasu na zuwa ne, kasa da sa’o’i 24 bayan da hukumar zabe ta kasa INEC ta sanar da cewa zaben gwamnan jihar bai kammala ba.

Jam’iyar PDP ta koka kan cewa an yi mata ba dai-dai ba inda ta nemi da a bayyana dan takararta,Ademola Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaben tunda shine wanda ya samu ƙuri’u mafi rinjaye.

A cikin yan tawagar shugaban majalisar dattawan a zuwa gidan jagoran jam’iyar ta SDP akwai Sanata Abiodun Olujimi daga jihar Ekiti da kuma Doyin Okupe daraktan yada labaran yakin neman zaben Saraki.

Ganawar na da nasaba da shirye-shiryen yadda za a hada karfi da karfe wajen kayar da jam’iyar PDP a zaben gwamnan jihar da za a sake yi a wasu mazabu ranar Alhamis.

Omisore ya amince yin aiki tare da Adeleke domin cigaban jihar.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...