Zaben cike gurbin jihar Kogi: An kashe barayin akwatin zabe biyu

[ad_1]








Aƙalla mutane biyu aka kashe lokacin zaben cike gurbi na kujerar dan majalisar wakilai dake wakiltar mazabar Kogi/Lokoja.

A jiya Asabar ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Ƙasa wato INEC ta gudanar da zaben cike gurbi a mazabar.

Zaben da aka fara gudanar da shi cikin tsanaki da kwanciyar hankali inda aka samu fitowar jama’a sosai amma daga bisani rikici ya dabaibaye zaben.

Wasu mutane da ake zargin yan bangar siyasa ne sun rika bi tashohin zabe suna tayar da hankali tare da tafka magudin zaɓe.

William Aya, mai magana da yawun rundunar Æ´ansandan jihar Kogi ya ce an kashe wani mutum mai suna, Yadau Umoru a tashar zabe ta Unguwan Pawa dake kusa da Fadar Maigari lokacin da yake kokarin satar akwati.

Ya ce an ajiye gawar mamacin a cibiyar kula da lafiya ta tarayya dake Lokoja.

An kuma kashe wani mutum da ba a tantance waye shiba a tashar zabe da kusa da ofishin rarraba hasken wutar lantarki shiyar Abuja dake Lokoja lokacin da yake kokarin gudu da akwatin a zaɓe.

Aya ya ce har ya zuwa yanzu ba a iya gane mutumin ba.

Tuni jam’iyar PDP dama wasu jam’iyu suka yi kira da a soke zaben.




[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...