[ad_1]
Aƙalla mutane biyu aka kashe lokacin zaben cike gurbi na kujerar dan majalisar wakilai dake wakiltar mazabar Kogi/Lokoja.
A jiya Asabar ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Ƙasa wato INEC ta gudanar da zaben cike gurbi a mazabar.
Zaben da aka fara gudanar da shi cikin tsanaki da kwanciyar hankali inda aka samu fitowar jama’a sosai amma daga bisani rikici ya dabaibaye zaben.
Wasu mutane da ake zargin yan bangar siyasa ne sun rika bi tashohin zabe suna tayar da hankali tare da tafka magudin zaɓe.
William Aya, mai magana da yawun rundunar ƴansandan jihar Kogi ya ce an kashe wani mutum mai suna, Yadau Umoru a tashar zabe ta Unguwan Pawa dake kusa da Fadar Maigari lokacin da yake kokarin satar akwati.
Ya ce an ajiye gawar mamacin a cibiyar kula da lafiya ta tarayya dake Lokoja.
An kuma kashe wani mutum da ba a tantance waye shiba a tashar zabe da kusa da ofishin rarraba hasken wutar lantarki shiyar Abuja dake Lokoja lokacin da yake kokarin gudu da akwatin a zaɓe.
Aya ya ce har ya zuwa yanzu ba a iya gane mutumin ba.
Tuni jam’iyar PDP dama wasu jam’iyu suka yi kira da a soke zaben.
[ad_2]