Zaben cike gurbin jihar Kogi: An kashe barayin akwatin zabe biyu

[ad_1]








Aƙalla mutane biyu aka kashe lokacin zaben cike gurbi na kujerar dan majalisar wakilai dake wakiltar mazabar Kogi/Lokoja.

A jiya Asabar ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Ƙasa wato INEC ta gudanar da zaben cike gurbi a mazabar.

Zaben da aka fara gudanar da shi cikin tsanaki da kwanciyar hankali inda aka samu fitowar jama’a sosai amma daga bisani rikici ya dabaibaye zaben.

Wasu mutane da ake zargin yan bangar siyasa ne sun rika bi tashohin zabe suna tayar da hankali tare da tafka magudin zaɓe.

William Aya, mai magana da yawun rundunar ƴansandan jihar Kogi ya ce an kashe wani mutum mai suna, Yadau Umoru a tashar zabe ta Unguwan Pawa dake kusa da Fadar Maigari lokacin da yake kokarin satar akwati.

Ya ce an ajiye gawar mamacin a cibiyar kula da lafiya ta tarayya dake Lokoja.

An kuma kashe wani mutum da ba a tantance waye shiba a tashar zabe da kusa da ofishin rarraba hasken wutar lantarki shiyar Abuja dake Lokoja lokacin da yake kokarin gudu da akwatin a zaɓe.

Aya ya ce har ya zuwa yanzu ba a iya gane mutumin ba.

Tuni jam’iyar PDP dama wasu jam’iyu suka yi kira da a soke zaben.




[ad_2]

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...