Zaben 2027 Zabe ne Tsakanin ‘Yan Najeriya Da Azzalumai — Oyegun

Shugaban Kwamitin Tsare-tsare da Manufofi na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), John Odigie-Oyegun, ya bayyana cewa babban zaɓen shekarar 2027 zai kasance fafatawa ne tsakanin ‘yan Najeriya da masu danniya.

Oyegun ya faɗi hakan ne a ranar Juma’a yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise TV, inda yake amsa tambayoyi kan siyasar ƙasar.

Ya ce da zuwan ADC, ba za a ci gaba da tafiyar da siyasa kamar yadda aka saba ba, yana mai jaddada cewa kowa na son ganin sauyi a ƙasar.

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa ya ƙara da cewa akwai babbar sadaukarwa da kowane ɓangare na al’umma ke yi a cikin ADC domin ganin an samu canji.

More from this stream

Recomended