Za’a Gina Tashar Motoci Ta Zamani A Obolo Afor Dake Jihar Enugu

[ad_1]

Tashar ta farko za’a ginata ne a garin Obollo-Afor dake jihar Enugu, inda tuni aka samu katafaren fili mai tsawon kadada 16, kuma zata dauki dukkan manyan motoci da kan tsaya a garuruwan dake kan manyan hanyoyin da hakan kan haddasa cunkoso da ma hatsari,.

Wakili a hukumar kula da wadannan tashoshi Injiniya K.C. Izuwah yace ya kamata gwamnatin Nigeria ta kafa duka a zata tilasta direbobi su rika tsayawa don hutawa; don an gano yawancin direbobin kan yi barcin sa’a 4 ne kacal cikin sa’o’I 24 inji Injiniya Chidi K.C. Izuwah.

Ya ci gaba da cewa akwai bukatar samar da tashoshin madakatar manyan motocin domin direbobi su samu su huta a kuma kaucewa hadarin da kan faru a kan hanyoyi sanadiyar ajiye manyan motocin a gefen tituna

Izuwah ya ce tashoshin na zamani za su zama da masaukan baki,gidajen abinci, bankuna, asibitoci, kotuna, wuraren ibada, makanikai har ma da wajen shakatawa da wanke motoci.

Shugaban hukumar zirga-zirgar harkar kasuwanci ta jiragen ruwa Hassan Bello, ya ce za a fara aikin nan take kuma za a kafa irin tashoshin a duk garuruwan da manyan motoci ke tsayawa, baya ga rage hatsaari, zai kuma bunkasa tattalin arzikin al’ummar yankunan.

Kungiyar direbobi da ake kira NURTW a takaice data masu manyan motocin sufuri wacce ake kira NARTO a takaice, sun amince da shiga wannan tsari don inganta rayuwar direbobin da kula da lafiyar motocin.

A saurari rahoton Nasiru Adamu El-Hikaya

[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...