Za a Bude Makarantu Ga Dalibai a Najeriya Domin Yin Jarrabawar WAEC

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa za a bude makarantu a ranar 4 ga watan Augusta ga daliban da ke ajin karshe a makarantun Sakandare domin rubuta jarrabawar WAEC.

Gwamnatin ta bayyana matakin ne a cikin watan sanarwar da ma’aikatar ilimi ta fitar a yau Litinin wacce ke dauke da sa hannun daraktan yada labarai na Ma’aikatar, Ben Bem Goong.

Wannan matakin ya biyo bayan shafe sa’o’i ana tattaunawa a yau tsakanin ma’aikatar ta ilimi da kwamishinonin ilimi da kuma masu ruwa da tsaki a harkokin ilimi a kasar.

Sanarwar ta bayyana yadda aka umarci ‘yan ajin karshe da su koma makaranta da an kammala bikin sallah mai zuwa domin shirin yin jarrabawar wacce za a fara a ranar 17 ga watan Augusta.

A tattaunawar tasu, an Kuma bayyana cewa makarantu za su bukaci taimako daga gwamnatin tarayya wajen iya budewa cikin gaggawa.

Makarantu a kasar daga matakin farko zuwa karshe sun shafe watanni a garkame saboda kokarin takaita yaduwar cutar Coronavirus.

A cikin makonnin da suka gabata gwamnatin ta bayyana cewa ba za a gudanar da jarrabawar WAEC ba saboda cutar, amma yanzu gwamnatin ta sauya matsayarta.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...