Yunwa da ƙishirwa na yi wa ƙananan yara barazana a Gaza

A yayin da Isra’ila ke ci gaba da kai munanan hare-hare a Gaza, ƙananan yara na cikin wadanda abin ya fi shafa.

Baya ga haka rashin ruwan sha da abinci na ci gaba da yin barazana.

“Abin da muke gani a Gaza a yanzu shi ne kisan gillar da ake yi wa kananan yara a hankali,” in ji Alexandra Saieh, shugabar manufofin agaji da bayar da shawarwari a kungiyar Save the Children International.

Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce yara shida ne suka mutu a arewacin Gaza sakamakon rashin ruwa da rashin abinci mai gina jiki a asibitocin Kamal Adwan da al-Shifa, yayin da wasu ke cikin mawuyacin hali.

More News

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...

Gwamnati za ta fara biyan ma’aikata naira 30,000 mafi ƙarancin albashi a Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya sanar da cewa za su fara aiwatar da tsarin mafi ƙarancin albashi naira 30,000 ga ma'aikatan jihar...