Yawan mutanen da suka mutu a hatsarin kwale-kwalen jihar Niger ya kai 42

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta jihar Niger NSEMA ta ce yawan mutanen da suka mutu a hatsarin kwale-kwale da ya faru a jihar sun kai mutum 42.

A ranar 1 ga watan Oktoba ne jirgin kwale-kwalen dake ɗauke da mutane sama da 300 akan hanyarsu ta zuwa wurin Maulidi  ya kife dasu a Gbajibo dake ƙaramar hukumar Mokwa ta jihar.

Tun bayar faruwar lamarin ne hukumar ta NSEMA da wasu sauran hukumomin bada agajin gaggawa suka duƙufa aikin ceto inda suka samu nasarar ceto sama da mutane 150.

Ibrahim Hussaini mai magana da yawun hukumar ta NSEMA ya ce an samu gano Æ™arin gawarwaki shida da safiyar ranar Juma’a.

“Daga Æ™arfe 6 na yammacin jiya zuwa 10 na safiyar yau Æ™arin gawarwaki 6 aka gano hakan ya sa jimilllar gawarwakin ya kai 42,” ya ce

A ranar Alhamis ne shugaban ƙasa Bola Ahmad ya bawa hukumar dake lura da ruwayen Najeriya da ta binciko dalilin da yasa ake yawan samun yawan faruwar hatsarin kwale-kwale a jihar.

More News

TCN na ci gaba da ƙoƙarin gyaran wutar lantarkin da ta lalace kwana biyu

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya sanar da ci gaban da aka samu wajen farfado da rukunin wutar kasa bayan wata tangardar...

Magoya bayan jam’iyyar NNPP sun Æ™ona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

PDP ta É—auki hanyar warware rikicin jam’iyyar

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya ce  an kawo karshen rikicin cikin gida da ya dabaibaye jami'yar PDP. Mohammed wanda shi ne shugaban Æ™ungiyar gwamnonin...

Dakarun Najeriya sun cafke wasu Æ´an’aiken Æ´anbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...