Yaushe Shugaba Buhari zai koma Najeriya?

Fadar Shugaban Najeriya ta ce sai ranar Asabar shugaban kasar zai koma gida bayan kammala hutun aiki da ya dauka.

Shugaban ya tafi birnin Landan ne domin hutun kwana 10, da ya fara a ranar 3 ga watan Agusta.

A farkon wannan makon ne wasu jaridun kasar suka bayyana cewa shugaban ya dage ranar da zai koma Najeriya, inda zai wuce kwanaki goma kamar yadda aka bayyana tun da farko.

To sai dai fadar shugaban ta musanta rahotannin.

Mai taimakawa shugaban na musamman kan yada labarai Malam Garba Shehu ya shida wa BBC cewa a ranar Asabar shugaban zai koma gida.

 

Garba Shehu ya ce Buhari zai yi kwanaki goma ne da ake aiki a cikinsu, don haka ba za a lissafa da Asabar da Lahadi da ke cikin makonnin da ya yi hutun ba a lissafi.

A bara dai Shugaba Buhari ya shafe watanni yana hutu a birnin Landan, abin da ya janyo ce-ce-ku-ce a kasar.

Shugaba Buhari mai shekara 76 zai sake tsaya takarar neman shugabancin kasar a zabukan da za a yi a watan Fabrairun badi.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...