Yau Mahajjatan Bana Suke Hawan Arafat A Saudiyya.

[ad_1]

Kimanin alhazai kamar miliyan daya da rabi zuwa miliyan biyu ake kyatata zaton suke aikin hajjin bana a kasa mai starki, Saudiyya.

Wakilin Sashen Hausa dake Saudiyya Abdulwaba Muhammad, ya tabbatar da adadin mhajjjatan bana a kasa mai tsarki.

Sai dai a wannan lokacin, wani abun da ba saban yake faruwa ya auku. An yi ruwan sama kamar da bakin kwarya tare da iska mai karfi a birnin Makka. Saboda tsananin ruwa da iska sai da aka dakatar da wasu abubuwa a masallacin Makka. Baicin hakan, ruwan ya kawar da wasu abubuwa da dama kamar gidaje da bishiyoyi, lamarin da ya shafi harkar saye da sayarwa. Iskar ta yi fatali da wasu kayayyakin da aka kasa domin sayarwa.

Dangane da shirin hawan arfa, tun misalin karfe goma na daren Nigeria jiya Lahadi aka fara kai mahajjatan. Dangane da tsaro mahukuntan kasar sun girke jami’ansu walau a masallatai ko kan hanyoyi ko kuma wuraren da jama’a suke taruwa.

Gameda mahajjata daga Nigeria kowace jiha tana iyakar kokarinta, wajen jigilar alhazansu zuwa wuraren da suka kamata cikin motocin safa safa.

A saurari firar da aka yi da Abdulwahab Muhammad

[ad_2]

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...