Yau ce rana ta ƙarshe ta jigilar maniyyata zuwa Saudiyya

Ranar Litinin din nan ce ranar da hukumomin ƙasar Saudiyya suka tsayar mastayin ranar cikar waadin kammala jigilar maniyyata aikin Hajjin bana daga kowace kusurwa ta duniya.

Da karfe 12 na tsakar daren yau Litinin agogon Saudiyya ne hukumomin na Saudiyya suka ce za su rufe filayen jiragen saman ƙasar 6 ga saukar duk wani jirgin da ya dauko maniyyata daga kowace kasa ta duniya.

Hakan ya sa ƙasashe musamman waɗan da ke da adadi mafi yawa na maniyyatan da ke rige-rigen ganin sun kammala jigilar maniyyatansu kafin cikar wa’adin.

Filayen jiragen su ne waɗan da aka keɓe domin jigilar maniyyatan na bana da ke biranen Riyadh, da Jiddah, da Madina, da Dammam, da Taif, da kuma Yanbu’u.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...