‘Yar gudun hijra ta haifi ‘yan hudu a Zamfara

[ad_1]

Dubban mutane sun rasa muhallansu a Najeriya

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Wata ‘yar gudun hijra Zainab Salisu mai kimanin shekara 33 da haihuwa, ta haifi ‘yan hudu a sansanin ‘yan gudun hijra na Maradun da ke jihar Zamfara.

Kamfanin dillancin labarai na NAN, ya rawaito cewa matar, Zainab, ta haifi maza biyu mata biyu a ranar Lahadin da ta gabata ba tare da wata matsala ba.

Mai jegon ta je sansanin ‘yan gudun hijrar ne daga kauyen Gidan Dan-Guntu da ke gundumar Maradun.

Mahaifin jariran Malam Salisu Muhammad, ya shaida wa manema labarai cewa sau daya tal matar tasa ta je asibiti domin awo.

Ya ce duk da ya ke ba ta samu wata matsala ba a yayin da ta ke dauke da cikin, ya so ta rinka zuwa awo akai- akai, amma kuma saboda fargabar hare-haren da mahara ke kai wa ba je ba in banda sau daya.

Malam Salisu, ya ce duk da lafiyar ta lau ba ta fuskantar wata matsala a yayin da ta ke dauke da juna biyun, sun lura cewa girman cikin ya yi yawa, amma kuma da ya ke ba haihuwar fari bace, sai ba su damu sosai ba, saboda ta taba haifar ‘yan biyu ma.

Mahaifin jariran, ya ci gaba da cewa da haihuwar ta zo sam bata jima tana nakuda ba, kuma ta samu taimakon ungozumomi ne a sansanin a yayin haihuwar.

Ya ce, ko da ta haifi jariran ‘yan hudu, sai jami’an da ke kula da sansanin suka dauki matar da jariran zuwa asibitin kwararru na Yariman Bakura da ke Gusau babban birnin jihar ta Zamfara domin za ta fi samun kulawa sosai.

Rahotanni sun ce Zainab da mijinta na daga cikin ‘yan gudun hijra fiye da dubu 12 da suka bar muhallansu saboda hare-haren da ake yawan kai wa a wasu yankunan jihar da suka hada da Maru da Maradun da Zurmi da Shinkafi da kuma Anka.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Karanta wasu karin labaran

[ad_2]

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...