Rahotanni daga jihar Borno sun tabbatar da cewa yanzu haka ana kan bata-kashi tsakanin sojojin Nijeriya da ‘yan Boko Haram a garin Damasak dake jihar Borno.
Wani mazaunin yankin ya tabbatarwa da jaridar RARIYA cewa an soma musayar wutar ne tsakanin sojoji da ‘yan ta’addan tun wajen karfe bakwai na daren yau. Inda mazauna yankin suke ta yin gudun hijira suna barin garin domin cetar da rayuwarsu.