‘Yansanda Sun Tsare Jami’ansu Uku Bisa Zargin Kisan Wani Da Ake Zargi Da Sata a Jihar Kebbi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi ta sanar da tsare wasu jami’anta uku bisa zarginsu da hannu a kisan wani da ake zargi da sata a garin Jega.

Mai magana da yawun rundunar, CSP Nafi’u Abubakar, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar a Birnin Kebbi.

A cewar sanarwar, lamarin ya samo asali ne daga rahoton satar tayoyin babbar mota da wani ya kai ofishin ‘yan sanda na Division a Jega.


CSP Abubakar ya jaddada cewa rundunar tana jajirce wajen tabbatar da bin ka’idoji da dabi’un aikin dan sanda.

More from this stream

Recomended