
Rundunar ƴan sandan jihar Ebonyi ta ce jami’anta sun kama Anya Baron-Ogbonnia jami’in gudanarwar cibiyar Amasiri Development Center dake Afikpo da kuma wasu sarakunan gargajiya biyu kan kisan mutane huɗu da aka yi a karamar hukumar Edda ta jihar.
Joshua Okandu mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya ce masu sarautar gargajiya sun Onyaidam Bassey da Godfrey Oko-Obia.
Ukandu ya ce an yi kamen ne bayan wani samame tare da haɗin gwiwar jami’an tsaron soja, DSS da kuma na Civil Defense.
Mai magana da yawun rundunar ya ce tunda farko an kama wasu mutane 10 a ya yin da ake cigaba da gudanar da bincike
A watan da ya wuce ne rikicin gonakin ya barke a tsakanin al’ummomin Okporojor dake Osso Edda a karamar hukumar Edda da kuma makotansu na Amasiri a karamar hukumar Afikpo.
Rikicin ya yi tsamari a ranar 29 ga watan Janairu bayan wasu dake dauke da makamai sun kai farmaki kauyen Okporojor inda suka kashe mutane huɗu tare da lalata gidaje da dama. Rahotanni sun bayyana cewa an fille kan mutane uku daga cikinsu.

