Yan sanda sun ceto wasu ƴan mata daga gidan karuwai

Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra sun ceto wasu ‘yan mata biyu da ba su kai shekaru 18 ba, wadanda ake amfani da su wajen karuwanci a wani samame da suka kai wani otel a unguwar Oba, karamar hukumar Idemili ta kudu a jihar.

An yi wannan farmakin ne biyo bayan wani bayani daga wani mai fallasa bayan an ci gaba da gudanar da ayyukan assha a kusa da otal din.

An ce za a kai ‘yan matan asibiti domin a duba lafiyarsu.

Da take jawabi jim kadan bayan kai farmakin a ranar Laraba, kwamishiniyar kula da harkokin mata da jin dadin jama’a ta jihar Ify Obinabo, ta yaba da kokarin jami’an tsaro wajen taimakawa wajen ceto ‘yan matan.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...