Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra sun ceto wasu ‘yan mata biyu da ba su kai shekaru 18 ba, wadanda ake amfani da su wajen karuwanci a wani samame da suka kai wani otel a unguwar Oba, karamar hukumar Idemili ta kudu a jihar.
An yi wannan farmakin ne biyo bayan wani bayani daga wani mai fallasa bayan an ci gaba da gudanar da ayyukan assha a kusa da otal din.
An ce za a kai ‘yan matan asibiti domin a duba lafiyarsu.
Da take jawabi jim kadan bayan kai farmakin a ranar Laraba, kwamishiniyar kula da harkokin mata da jin dadin jama’a ta jihar Ify Obinabo, ta yaba da kokarin jami’an tsaro wajen taimakawa wajen ceto ‘yan matan.