‘Yan Sanda Na Ci Gaba Da Tsare Dan Jaridar Premium Times

[ad_1]

Har yanzu ‘yan sandan Nigeria na ci gaba da tsare dan jaridar Premium Times Samuel Ogundipe wanda suka cafke akan wani rahoton da shugaban ‘yan sandan ya rubuta akan mamayar da jami’an DSS suka yiwa majalisun kasar ya kuma mikawa mukaddashin shugaban kasa amma da dan jaridar ya buga a jarida.

Rahoton baban sifeton ya bayyana irin rawar da shugaban hukumar DSS Malam Lawal Daura ya taka abun da kuma ya kaiga tubesh daga mukaminsa.

Ta bakin kakakin babban sifeton ‘yan sandan Nigeria Bala Ibrahim abun da dan jaridar ya yi ya sabawa irin horon da ake baiwa ‘yan jarida a kasar. Ya na cewa wani abun idan aka fada yana iya tada zaune tsaye ko ma hambare gwamnatin dake ci. Saboda haka ba karamar magana ba ce.

Sai dai duk da ikirarin kakakin babban sifeton, kungiyar Amnesty International ta yi watsi da abubuwan da ya fada. Kakakinta Malam Isa Sanusi ya ce duk maganar ana son a razana ‘yan jarida ne domin su tsorata, su gaza yin aikinsu cikin walwala da lumana. Duk maganar da ‘yan sandan ke yi shirmen banza ne kawai, injishi.

Ita ma kungiyar ‘yan jaridar Nigeria wato, NUJ, ta rubuta wata wasika da kakkausar lafazi zuwa ga mukaddashin shugaban Nigeria ya sa baki domin ‘yan sanda su sako dan jaridar Samuel Ogundipe.

Sha’aibu Usman Liman sakataren ‘yan jaridar Nigeria ya ce idan za’a je kotu ne a yi shari’a yadda ta dace kungiyarsu ba ta da matsala da hakan. Amma a daina kama ‘yan jarida ana musguna masu kafin a kaisu kotu. Ya ce hakan ba daidai ba ne.

Amma kakakin shugaban ‘yan sandan Nigeria Bala Ibrahim ya ce su basa rike dashi domin an kaishi kotu. Kotu ce za ta ce ya daina abun da ake tuhumarsa a kai ko kuma ta wankeshi a sakeshi.

Shi ma kamfanin Premium Times ta bakin wani babban jami’inta Malam Sani Tukur ya ce yaushe ‘yan sandan suka kaishi kotu, ko sun bi bayan fage ne? Ya ce dokar kasa ta ce duk wanda aka kama ya na da ikon ya nemi lauya saboda haka menene dalilin kaishi a boye?

A saurari rahoton Hassan Maina Kaina

[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...