Rahotanni sun nuna cewa ’yan Najeriya da dama sun bayyana ra’ayoyinsu kan yawaitar tafiye-tafiyen shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zuwa kasashen waje.
An ruwaito cewa shugaban ya shafe kwanaki 23 a kasashen ketare cikin watan Janairun 2026 kadai, bayan ya bar Najeriya tun ranar 28 ga Disambar 2025 zuwa Turai.
Shugaban ya yi kwanaki tara a kasar Faransa domin hutun karshen shekara. Daga nan ya wuce Abu Dhabi a Hadaddiyar Daular Larabawa, inda ya halarci taron Makon Dorewar Muhalli na 2026 na tsawon kwanaki bakwai. Haka kuma ya kai ziyarar aiki kasar Turkiyya inda ya sake shafe kwanaki shida kafin dawowa gida.
Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, na cikin wadanda suka soki yawan tafiye-tafiyen shugaban. Ya ce kwanaki 23 da aka shafe a waje cikin wata guda abin damuwa ne, musamman duba da kalubalen tsaro da tattalin arziki da ake fuskanta.
Wasu ’yan Najeriya ma sun bayyana mabanbantan ra’ayoyi kan lamarin.
’Yan Najeriya Suna Nuna Fushinsu Kan Yawan Tafiye-Tafiyen Tinubu Zuwa Kasashen Waje

