[ad_1]
Aƙalla mutane 10 ne suka mutu biyo bayan wani harin kunar bakin wake biyu a wani wuri dake cike da jama’a a ƙaramar hukumar Madagali ta jihar Adamawa.
Mazauna garin sun shedawa jaridar Daily Trust cewa mata biyu ne suka tayar da bom din dake jikinsu ta bangaren da ake shiga garin daga Gwoza.
Wani mazaunin garin mai suna, Aura Garga ya fadawa jaridar cewa yan kunar bakin waken sun kai harin da misalin 12 na ranar Asabar inda suka kashe kansu da kuma wasu mutane 10.
Ya ce an kwashe da yawa daga cikin mutanen da suka jikkata ya zuwa asibiti domin samun kulawa.
Jaridar ta gaza jin ta bakin hukumomin soji dake bataliya ta 28 dake Mubi.
Garin Madagali dake da tazarar kilomita 250 daga Yola babban birnin jihar Adamawa ya dade yana fuskantar hare-hare tun bayan da aka samu nasarar kwato garin daga hannun yan Boko Haram a shekarar 2015.
[ad_2]