
Hukumar Zabe ta Kasa INEC ta ce ba gaskiya bane rahotannin dake cewa tayi wani shiri na musamman da zai bawa yan gudun hijira dake wajen kasarnan damar yin zabe.
A wata sanarwa kwamishinan wayar da kan masu kada kuri’a da sadarwa na hukumar ya ce yan kasar waje baza su yi zabe ba a shekarar 2019.
Sanarwar ta ce yan gudun hijira da yanzu suke zaune ba a jihar da suka yi rijista ba, to za suyi zaben shugaban kasa ne kawai.
Jam’iyar adawa ta PDP dai tayi zargin cewa hukumar zaben na shirin tafka magudi a zaben shekarar 2019 ta hanyar bude wasu tashoshin zabe , a makotan kasashe.
Jam’iyar ta ce hukumar za ta bude tashoshin zaben ne a kasashen Kamaru da kuma Nijar.