‘Yan Gudun Hijira Daga Zamfara Sun Bayyana Abun Da Ya Addabesu

[ad_1]

Malam Muhammad Isa mai magana da yawunsu y ace barayi ne da suka yi shigar Fulani, dauke da bindigogi suka farmasu.

Barayin akan kimamin babura talatin, kowane dauke da bindiga samfurin AK-47. Duk garin da suka shiga suna tarwatsa mutane, kuma duk wanda ya fito sai su harbeshi kana su yi awon gaba dabbobin garin.

Malam Muhammad Isa daya daga cikin dubban talakawa daga jihar Zamfara da suka fake a jihar Katsina, ana dab da yin sallah yace barayin sun shiga garinsu ne da misalin karfe daya na dare basu kuma bar garin ba sai wajejen karfe hudu na asuba.

Yace sun yi amfani da bindiga mai sarafa kansa suka yi ta harbe harbe. A cikin yamutsin da ya faru an kashewa Malam Isa kani, wanda ya bar mata biyu da ‘ya’ya goma. Yanzu dai bai san inda sauran ‘yanuwansu suke ba.

Wannan abun da ya faru ya sa Malam Isa daukar mahaifiyarsa zuwa birnin Katsina.

Akwai dubban wasu ‘yan asalin jihar Zamfara dake gudun hijira a karamar hukumar Kankara cikin jihar ta Katsina.

Babangida Murtala wani ganau y ace yawancin mutanen da suke neman mafaka a Katsina mata ne da yara kanana wadanda suke cikin wani halin bantausayi.

Kakakin gwamnan jihar Katsina Abdu Labarn Manunfashi ya tabbatar cewa gwamnatin jihar Katsina ta san da zaman ‘yan gudun hijiran a jihar. Yace gwamnatin ce ta basu wata makaranta su zauna ciki, da kuma basu

Gwamnan jihar Aminu Bello Masari ya kai masu ziyara, ya yi alkawarin cewa gwamnati za ta ci gaba da taimaka masu, kana ya yi gargadi jama’ar dake kusa dasu su dinga taimaka masu.

A saurari rahoton Hassan Maina Kaina

[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...